Mattiyu
1
Asalin Yesu Kiristi
(Luka 3.23-38)
Tarihin da aka rubuta game da asalin Yesu Kiristi ɗan Dawuda, ɗan Ibrahim.
 
Ibrahim ya haifi Ishaku,
Ishaku ya haifi Yaƙub,
Yaƙub ya haifi Yahuda da ’yan’uwansa,
Yahuda ya haifi Ferez da Zera, waɗanda Tamar ce mahaifiyarsu;
Ferez ya haifi Hezron,
Hezron ya haifi Ram,
Ram ya haifi Amminadab,
Amminadab ya haifi Nashon,
Nashon ya haifi Salmon,
Salmon ya haifi Bowaz, wanda Rahab ce mahaifiyarsa,
Bowaz ya haifi Obed, wanda Rut ce mahaifiyarsa,
Obed ya haifi Yesse,
Yesse kuwa ya haifi Sarki Dawuda.
 
Dawuda ya haifi Solomon, wanda matar Uriya ce mahaifiyarsa.
Solomon ya haifi Rehobowam,
Rehobowam ya haifi Abiya,
Abiya ya haifi Asa,
Asa ya haifi Yehoshafat,
Yehoshafat ya haifi Yehoram,
Yehoram ya haifi Azariya,
Azariya ya haifi Yotam,
Yotam ya haifi Ahaz,
Ahaz ya haifi Hezekiya,
10 Hezekiya ya haifi Manasse,
Manasse ya haifi Amon,
Amon ya haifi Yosiya,
11 Yosiya kuma ya haifi Yekoniya* Wato, Jehohiyachin; haka ma a aya 12 da ’yan’uwansa a lokacin da aka kwashe su zuwa bauta a Babilon.
 
12 Bayan an kwashe su zuwa bauta a Babilon.
Yekoniya ya haifi Sheyaltiyel,
Sheyaltiyel ya haifi Zerubbabel,
13 Zerubbabel ya haifi Abiyud,
Abiyud ya haifi Eliyakim,
Eliyakim ya haifi Azor,
14 Azor ya haifi Zadok,
Zadok ya haifi Akim,
Akim kuma ya haifi Eliyud,
15 Eliyud ya haifi Eleyazar,
Eleyazar ya haifi Mattan,
Mattan ya haifi Yaƙub,
16 Yaƙub ya haifi Yusuf, mijin Maryamu, wadda ta haifi Yesu, wanda ake kira Kiristi.
 
17 Ta haka akwai zuriya goma sha huɗu ke nan duka-duka daga lokacin Ibrahim zuwa lokacin Dawuda, goma sha huɗu kuma daga Dawuda zuwa bauta a Babilon, goma sha huɗu kuma daga bauta a Babilon zuwa Kiristi. Ko kuwa Kiristi. Kiristi (Da Girik) Almasihu (Da Ibraniyanci) duk suna nufin “Shafaffe.”
Haihuwar Yesu Kiristi
(Luka 2.1-7)
18 Ga yadda haihuwar Yesu Kiristi ta kasance. An yi alkawarin auren mahaifiyarsa Maryamu, ga Yusuf. Amma tun kafin su zama miji da mata, sai aka tarar Maryamu tana da ciki, ta wurin Ruhu Mai Tsarki. 19 Yusuf mijinta, da yake shi mai adalci ne, bai so yă ba ta kunya, yă tone mata asiri a fili ba, sai ya yi tunani yă sake ta a ɓoye.
20 Amma yana cikin wannan tunani, sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana masa cikin mafarki ya ce, “Yusuf ɗan Dawuda, kada ka ji tsoron ɗaukan Maryamu zuwa gidanka a matsayin matarka, gama cikin nan nata, daga wurin Ruhu Mai Tsarki ne. 21 Za tă haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu, Yesu da Girik shi ne Yoshuwa da Ibraniyanci, wanda yake nufin Ubangiji yana ceto. gama shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.”
22 Duk wannan ya faru ne, don a cika abin da Ubangiji ya faɗi ta bakin annabin cewa, 23 “Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, kuma za a kira shi Immanuwel”§ Ish 7.14 (wanda yake nufin “Allah tare da mu”).
24 Da Yusuf ya farka daga barci, sai ya bi umarnin mala’ikan Ubangiji, ya ɗauki Maryamu zuwa gida a matsayin matarsa. 25 Amma bai kwana da ita ba, sai bayan da ta haifi ɗan. Ya kuwa sa masa suna Yesu.

*1:11 Wato, Jehohiyachin; haka ma a aya 12

1:17 Ko kuwa Kiristi. Kiristi (Da Girik) Almasihu (Da Ibraniyanci) duk suna nufin “Shafaffe.”

1:21 Yesu da Girik shi ne Yoshuwa da Ibraniyanci, wanda yake nufin Ubangiji yana ceto.

§1:23 Ish 7.14